Connect with us

Ilimi

Hukumar Hisbah Ta Ziyarci Majalisar Dokokin Kano

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar tabbatar da ingantattun tsare-tsare na walwala ga ma’aikatan Hisba domin tabbatar da samar da ayyuka masu inganci.

 

 

Mamba mai wakiltar mazabar Minjibir, Alhaji Abdulhamid Abdul ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin mataimakin babban kwamandan hukumar Hisba ta jihar Kano Dr Mujahideen Aminuddeen Abubakar a harabar majalisar da ke Kano.

 

Gwamnatin jihar ta kafa hukumar Hisbah ta jihar Kano a shekarar 2000 kuma an ingantata a shekarar 2003 tare da samar da jami’an tsaro na Hisbah.

 

Tun da farko Abdulhamid Minjibir ya dauki nauyin kudirin doka da ke kira ga sake duba albashi da alawus-alawus na Hukumar Hisba don shiga cikin ma’aikatan gwamnati.

 

Ya bayyana cewa saboda rawar da kwamitin ke takawa majalisar za ta duba batun gyaran dokar kafa hukumar Hisbah domin amincewar bangaren zartarwa daga baya.

 

“An gabatar da kudirin kuma an amince da shi kafin mika shi ga bangaren zartarwa za mu bi diddigin aiwatar da shi insha Allah”

 

Mataimakin Kwamanda, Dr Mujahideen Aminuddeen Abubakar ya yabawa mamba mai wakiltan Minjibir bisa hangen nesa wajen daukar nauyin kudirin.

 

Ya yi nuni da cewa hukumar Hisbah ta jihar Kano ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kokarin tsaftace Kano daga duk wani nau’i na munanan dabi’u.

 

Idan za a tuna a ranar Litinin 14 ga watan Oktoba 2024 memba mai wakiltar Minjibir Abdulhamid Abdul ke gabatar da kudirin yin kira ga majalisar dokokin jihar Kano da ta duba yiwuwar sake shigar da jami’an Hisbah cikin ma’aikatan jihar baya ga sake duba sunayensu da alawus-alawus.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

Labarai

Ilimi20 hours ago

Gwamnati Za Ta Yiwa Madatsar Ruwan Alau Garanbawul A Barno

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na yin garambawul tare da tabbatar da madatsar ruwa ta Alau da ke Maiduguri a...

Fasaha20 hours ago

Majalisar Zartaswar Jihar Jigawa Ta Fitar Kudaden Tallafin Karatu

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da kudi sama da naira miliyan dari bakwai da casa’in da takwas domin...

Labarai21 hours ago

Kungiyar Tsoffin Manyan Sakatarorin Zamfara Ta Sami Kyautar Mota

Gwamna Lawal Ya Ba Da Kyautar Mota Ga Ƙungiyar Tsaffin Manyan Sakatarorin Da Suka Yi Ritaya A Zamfara Gwamnan Jihar...

Labarai21 hours ago

An Tsinci Gawar Tauraron Mawakan One Direction Liam Payne

Liam Payne, ɗaya daga cikin mawaƙa a tawagar One Direction, ya mutu a Argentina bayan ya faɗo daga hawa na...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Wadanda Fashear Tankar Mai Ta Shafa A Jigawa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana matukar alhininsa dangane da mummunan fashewar tankar da ta afku a garin Majiya...

Ilimi22 hours ago

Hukumar Hisbah Ta Ziyarci Majalisar Dokokin Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar tabbatar da ingantattun tsare-tsare na walwala ga ma’aikatan Hisba domin tabbatar...

Fasaha22 hours ago

Za A Fafata A Gasar Tseren Doki Ta Masarautar Gwandu

Ana sa ran al’ummomin duniya daga Hadaddiyar Daular Larabawa da kasashen yammacin Afirka za su halarci gasar tseren doki na...

Kasuwanci22 hours ago

Gwamnan Niger Ya Kaddamar Da Shirin Kula da Lafiyar ‘Yan Fansho Da Tsofaffi

Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja ya kaddamar da kunshin inshorar lafiya, wani shiri da aka tsara don samar...

Labarai22 hours ago

Kamala Harris Ta Yi Alkawarin Sauya Salon Mulkin Amurka Idan Ta Lashe Zabe

Ƴar takarar shugabancin Amurka a jam’iyyar Democrat, Kamala Harris, ta yi alƙawarin sauya salo daga irin kamun ludayin shugaba Joe...

Labarai4 days ago

Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa

Jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta ce ba za ta yi takara a zaben  kananan hukumomi da za a gudanar...

Mafi Shahara