Labarai
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
Biyo bayan rushewar masallacin garin Damagaram na Jamhuriyar Nijar, Gwamna Dikko Umar Radda na jihar Katsina ya bayar da gudunmawar Dala dubu 10 domin sake gina masallacin.
Masallacin dai na da dadadden tarihi domin an gina shi ne tun shekaru 200 da suka wuce.
Gwamna Radda ya bayar da gudunmawar ne ta hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin siyasa, Alhaji Ya’u Umar Gwajo-gwajo, wanda ke rike da sarautar ‘Turakin Damagaram’.
Yayin da yake bayyana godiyarsa ga Gwamnan bisa gudunmawar, mai alfarma Sarkin Musulmin Damagaram, Sultan Umaru Sanda, yace tallafin zai taimaka matuka wajen sake gina masallacin.
Ya ce gudunmawar hakan za ta inganta dadaddiyar alakar da ke tsakanin jihar Katsina da masarautar Damagaram wadda ta kai shekaru 500.
A nasa jawabin, Alhaji Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya shaida wa Sultan Umaru Sanda cewa Gwamna Dikko Radda ya bada gudunmawar ne saboda inganta tarbiyyar addini a masarautar.
“Wannan masallacin zai taimaka wajen cusa tarbiyyar addinin Musulunci a cikin al’ummarmu, kuma hakan zai taimaka wajen magance matsaloli da dama a cikin al’umma.
“Mu al’umma daya ce da turawa suka raba tsakaninmu, shi ya sa ya kamata mu karfafa alakar da ke tsakanin al’ummarmu kuma mu hada kai wajen magance kalubalen da muke fuskanta baki daya,” inji Gwajo-gwajo.
Daga Isma’il Adamu
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar
-
Labarai4 days ago
Isra’ila Ta Lalata Wani Masallaci A Harin Lebanon