Connect with us

Labarai

An Yi Wa Mutum 3 Ɗaurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Kurma Fyaɗe

Published

on

Wata Babbar Kotu da ke zamanta a Birnin Kebbi ta yanke wa wasu mutum uku hukuncin ɗaurin rai da rai sakamakon samun su da laifin yi wa wata kurma mai shekara 18 fyaɗe.

Waɗanda aka yanke wa hukuncin su ne; Amiru Sani, Aliyu Umar, da Bashar Dan-Inno.

An same su da laifin haɗa baki da aikata fyaɗe a ƙauyen Wararin Zaromawa da ke ƙaramar hukumar Gwandu a jihar.

Mai gabatar da ƙara, ƙarƙashin jagorancin Faridah Muhammad, ta bayyana cewa mutanen sun kutsa gidan matar ne yayin da ta ke barci, suka ɗaure hannunta sannan suka yi mata fyaɗe.

Muhammad ta buƙaci kotu da ta zartar da hukuncin da ya wajaba kan waɗanda suka aikata laifin.

Ta bayyana cewar laifin ya saɓa da sashe na 259 da 60 na dokar manyan laifuka ta Jihar Kebbi ta 2021.

Mai kare waɗanda ake tuhuma, ya roƙi a kotun ta yi musu sassauci.

A hukuncin da ya yanke, mai shari’a Shamsudeen Jafar, ya bayyana cewa kotun ta gamsu da shaidun da aka gabatar mata cewar waɗanda ake tuhuma sun haɗa baki wajen aikata laifin.

Don haka alƙalin ya yanke wa kowannensu hukuncin ɗaurin rai da rai kamar yadda doka ta tanada.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Ilimi18 hours ago

Gwamnati Za Ta Yiwa Madatsar Ruwan Alau Garanbawul A Barno

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na yin garambawul tare da tabbatar da madatsar ruwa ta Alau da ke Maiduguri a...

Fasaha19 hours ago

Majalisar Zartaswar Jihar Jigawa Ta Fitar Kudaden Tallafin Karatu

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da kudi sama da naira miliyan dari bakwai da casa’in da takwas domin...

Labarai19 hours ago

Kungiyar Tsoffin Manyan Sakatarorin Zamfara Ta Sami Kyautar Mota

Gwamna Lawal Ya Ba Da Kyautar Mota Ga Ƙungiyar Tsaffin Manyan Sakatarorin Da Suka Yi Ritaya A Zamfara Gwamnan Jihar...

Labarai20 hours ago

An Tsinci Gawar Tauraron Mawakan One Direction Liam Payne

Liam Payne, ɗaya daga cikin mawaƙa a tawagar One Direction, ya mutu a Argentina bayan ya faɗo daga hawa na...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Wadanda Fashear Tankar Mai Ta Shafa A Jigawa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana matukar alhininsa dangane da mummunan fashewar tankar da ta afku a garin Majiya...

Ilimi20 hours ago

Hukumar Hisbah Ta Ziyarci Majalisar Dokokin Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar tabbatar da ingantattun tsare-tsare na walwala ga ma’aikatan Hisba domin tabbatar...

Fasaha20 hours ago

Za A Fafata A Gasar Tseren Doki Ta Masarautar Gwandu

Ana sa ran al’ummomin duniya daga Hadaddiyar Daular Larabawa da kasashen yammacin Afirka za su halarci gasar tseren doki na...

Kasuwanci20 hours ago

Gwamnan Niger Ya Kaddamar Da Shirin Kula da Lafiyar ‘Yan Fansho Da Tsofaffi

Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja ya kaddamar da kunshin inshorar lafiya, wani shiri da aka tsara don samar...

Labarai21 hours ago

Kamala Harris Ta Yi Alkawarin Sauya Salon Mulkin Amurka Idan Ta Lashe Zabe

Ƴar takarar shugabancin Amurka a jam’iyyar Democrat, Kamala Harris, ta yi alƙawarin sauya salo daga irin kamun ludayin shugaba Joe...

Labarai4 days ago

Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa

Jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta ce ba za ta yi takara a zaben  kananan hukumomi da za a gudanar...

Mafi Shahara