Labarai
An Yi Wa Mutum 3 Ɗaurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Kurma Fyaɗe
Wata Babbar Kotu da ke zamanta a Birnin Kebbi ta yanke wa wasu mutum uku hukuncin ɗaurin rai da rai sakamakon samun su da laifin yi wa wata kurma mai shekara 18 fyaɗe.
Waɗanda aka yanke wa hukuncin su ne; Amiru Sani, Aliyu Umar, da Bashar Dan-Inno.
An same su da laifin haɗa baki da aikata fyaɗe a ƙauyen Wararin Zaromawa da ke ƙaramar hukumar Gwandu a jihar.
Mai gabatar da ƙara, ƙarƙashin jagorancin Faridah Muhammad, ta bayyana cewa mutanen sun kutsa gidan matar ne yayin da ta ke barci, suka ɗaure hannunta sannan suka yi mata fyaɗe.
Muhammad ta buƙaci kotu da ta zartar da hukuncin da ya wajaba kan waɗanda suka aikata laifin.
Ta bayyana cewar laifin ya saɓa da sashe na 259 da 60 na dokar manyan laifuka ta Jihar Kebbi ta 2021.
Mai kare waɗanda ake tuhuma, ya roƙi a kotun ta yi musu sassauci.
A hukuncin da ya yanke, mai shari’a Shamsudeen Jafar, ya bayyana cewa kotun ta gamsu da shaidun da aka gabatar mata cewar waɗanda ake tuhuma sun haɗa baki wajen aikata laifin.
Don haka alƙalin ya yanke wa kowannensu hukuncin ɗaurin rai da rai kamar yadda doka ta tanada.
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar