Labarai
Tsohuwar Firaministar Bangladesh ta Ce za Ta koma Kasar
Ɗan tsohuwar firaministar Banglaesh, Sheikh Hasina, ya shaida wa kafar watsa labaran Indiya cewa mahaifiyarshi na shirin komawa ƙasar bayan sabuwar gwamnatin riƙon-ƙwarya ta tsayar da lokacin da za ta gudanar da zaɓe.
Sheikh Hasina, ta sauka daga muƙaminta tare da tserewa maƙwabciyar ƙasar Indiya a ranar Litinin bayan kwashe makonni ana zanga-zangar ƙin mulkinta.
An rantsar da gwamnatin riƙon ƙwaryar da Muhammad Yunus wanda ya taɓa samun kyautar Nobel ta zaman lafiya zai jagoranta a jiya Alhamis.
An kashe mutum sama da 400 a tarzomar da aka yi fama da ita a kasar, kafin hasina ta tsere, kuma yawancin wadanda suka mutu farar hula ne da jami’an tsaro suka harbe, to amma kum har da ‘yansanda a cikin wadanda suka rasu.
Tarzomar ta kasance rikici mafi muni da aka zubar da jini wanda ba a taba yi ba, tun bayan yakin da ya ki kasar ga samun ‘yancin kai a 1971.
BBC
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai7 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai7 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai7 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai5 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai7 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar