Labarai
Darajar Takardar Kuɗin Habasha Na Karyewa Bayan Matakan Hukumomi
Takardar kuɗin Habasha, Birr ta rasa kusan kashi ɗaya bisa uku na darajarta bayan da hukumomi suka sanar da tsarin kasuwa ta tantance darajar kuɗin ƙasar.
Matakin wani gagarumin tsari ne karon farko a kusan rabin ƙarni.
Matakin wani yunƙuri ne na garambawul ɗin da gwamnati ke yi wa tattalin arzikin ƙasar da ya janyo ɓudewar ƙofa ta kamfanonin sadarwa da ƙananan masu sana’oi ga masu zuba hannun jari na ƙasa da ƙasa.
Bankunan kasuwanci a Habasha a yanzu za su iya saye su kuma sayar da kuɗaɗen ƙasashen waje a tsakaninsu da kwastamominsu a kan farashin da suka yarje wa juna.
Babban bankin ya ce sauyin cike yake da ƙalubale amma ya zama dole sai dai ya ce a yanzu ba zai riƙa ƙayyade darajar kuɗin ƙasar ba.
A yanzu, Birr ta rasa kashi 30 cikin 100 na darajarta a kan kuɗin dala tun bayan sanarwar.
Kasar na tattaunawa da cibiyoyin da ke bayar da bashi domin a sake fasalta bashin ƙasar yayin da tsadar rayuwa da ƙarancin kuɗaɗen waje ke ci gaba da haifar da ƙalubale.
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai7 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai7 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai7 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai5 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai7 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar