Connect with us

Ilimi

Zamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi

Published

on

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da wani shirin gaggawa na kwanaki 120 da nufin magance manyan matsalolin da ke addabar ɓangaren ilimi a jihar.

An ɗauki wannan mataki ne a yayin taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 65, wanda gwamnan ya jagoranta a gidan gwamnati da ke Gusau.

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa an tattauna muhimman batutuwa da suka shafi ilimi, lafiya, ayyuka da sauran fannoni, inda aka amince da manyan tsare-tsare domin inganta ayyukan gwamnati a jihar.

Ya ce babban abin da ya fi jan hankali a taron shi ne amincewa da shirin farfaɗo da ilimi, wanda ya samo asali daga binciken da Ma’aikatar Ilimi da Hukumar Tabbatar da Ingancin Ilimi suka gudanar a baya.

A cewarsa, kwamishinan ilimi mai kula, Abdulmalik Abubakar Gajam, ne ya gabatar da shirin, wanda ya ƙunshi sauye-sauye na musamman cikin ƙayyadadden lokaci.

Shirin ya haɗa da tantance albashin ma’aikata, cikakken nazarin makarantu, da duba gine-ginen makarantu, tare da mayar da hankali kan inganta shugabanci da amfani da fasahar zamani, horar da malamai, da kuma kula da jin daɗin ɗalibai.

Haka kuma, majalisar ta amince da kafa wani kwamiti na haɗin gwiwa domin gano da kuma tantance gine-ginen da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a kusa da makarantu.

Sanarwar ta ce za a bai wa wannan kwamiti, wanda Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha za ta jagoranta, ikon cire ko matsar da irin waɗannan gine-gine domin samar da ingantaccen muhalli na karatu.

Bugu da ƙari, majalisar ta amince da ƙirƙirar dokar bai ɗaya da za ta shafi dukkan matakan ilimi daga kula da yara ƙanana har zuwa manyan makarantu.

An tsara wannan doka ne tare da haɗin gwiwar manyan masu ruwa da tsaki, ciki har da hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin farar hula, sarakunan gargajiya da abokan hulɗa na ci gaba, kuma za a miƙa ta ga majalisar dokokin jihar domin duba ta da kuma amincewa da ita cikin lokacin shirin gaggawar.

A matsayin wani ɓangare na gyare-gyaren da ake yi, kakakin gwamnan ya ƙara da cewa gwamnan ya amince da sauya wurin aiki ga ma’aikatan da ba malamai ba, kamar masu aike-aike, ma’aikatan tsafta, masu kula da lambun makaranta, masu girki, masu gadi, direbobi da ƙwararru, daga jerin albashin Ma’aikatar Ilimi zuwa wasu ma’aikatu ko kamfanoni masu zaman kansu.

Haka kuma, majalisar ta amince da kafa kwamitin jagoranci na jihar kan dokar ta-ɓaci a ɓangaren ilimi, tare da ba shi damar kafa ƙungiyar masu fasaha domin taimakawa aiwatar da shirin.

Aminu Dalhatu/Gusau

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara