Connect with us

Labarai

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

Published

on

 

By Adamu Yusuf

 

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki da ke kula da harkokin bala’o’i a Jihar Kaduna, sun sake haɗa karfi da karfe domin rage aukuwar bala’o’i a wannan shekarar.

 

Da yake magana a wajen taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a ofishin NEMA da ke Kaduna domin duba abubuwan da suka faru na bala’o’i a shekarar da ta gabata, Shugaban Ayyuka na hukumar NEMA mai kula da jihohin Katsina da Kaduna, Suleiman Mohammed, ya ce hukumar ta sauya tsarin aikin ta daga bayar da taimako gaggawa bayan bala’i ya faru zuwa ɗaukar matakan kare faruwar bala’i baki daya.

 

Ya bayyana cewa bayan hukumomin da suka dace kamar Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya sun fitar da hasashen yanayi na kakar daminan bana, hukumar NEMA ta shirya irin wannan taron masu ruwa da tsaki tun farkon shekarar domin nazarin yiwuwar illolin da ka iya tasowa tare da tsara hanyoyin da za a bi wajen shawo kan bala’o’i.

 

A cewarsa, taron ya haɗa manyan masu ruwa da tsaki da suka tattauna hanyoyin da za su yi aiki tare wajen tunkarar bala’o’i tun kafin su faru da lokacin da suke faruwa, da kuma bayan sun faru.

 

Suleiman Mohammed ya kuma bayyana cewa haɗin gwiwar hukumomi kamar Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA), Kungiyar Red Cross, Hukumar Kashe Gobara, Civil Defence da sauran hukumomi ya taimaka wajen magance wasu bala’o’i da suka faru a jihar a shekarar da ta gabata, ciki har da ambaliya, gobara da kuma hatsarin tankokin mai.

 

Ya tuna cewa an gudanar da wani atisayen kwaikwayo kan yadda za a magance hatsarin tankokin mai a Maraban Jos, domin nuna yanda hukumar take gudanar da ayyukan ceto da agajin gaggawa.

 

Ya ce, “Atisayen wanda ya haɗa da direbobin tankokin mai da sauran masu ruwa da tsaki, an shirya shi ne domin ƙarfafa shirin ko-ta-kwana da kuma tabbatar da haɗin gwiwar da ya dace idan irin waɗannan bala’o’i suka faru.”

 

Ya ƙara da cewa duk da cewa an samu wasu ambaliyar ruwa a yankuna kamar Kaduna North, Kaduna South, Zaria da kuma ƙaramar hukumar Sanga, saurin ɗaukar mataki da hukumomin agaji suka yi ya taimaka wajen rage illolin da bala’in ya jawo ga al’ummomin da abin ya shafa.

 

Shi ma da yake nasa jawabin, Shugaban Sashen Kula da Bala’o’i na Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Najeriya (NSCDC) a Jihar Kaduna, Mataimakin Kwamandan Hukumar Akaine King Michael, ya bayyana taron a matsayin mai muhimmanci kuma da ya zo a kan lokaci domin nazarin ayyukan kula da bala’o’i na shekarar da ta gabata.

 

Ya ce taron ya ba masu ruwa da tsaki damar tantance abubuwan da suka faru a shekarar 2025, musamman hatsarin tankokin mai da ke ɗauke da man fetur, wanda sau da dama kan haddasa zubar mai a kan hanyoyi tare da jefa rayuka da dukiyoyi cikin haɗari.

Michael ya kuma bayyana cewa hukumar NSCDC na ci gaba da aiki tare da NEMA wajen gudanar da ayyukan ceto yayin bala’o’i, inda ya ce babban aikin su shi ne fitar da mutanen da abin ya shafa daga wuraren haɗari, kulle wuraren da lamarin ya faru da kuma hana jama’a ɗiban mai idan tankar mai ta yi hatsari..

 

A nata jawabin, Shugabar Sashen Muhalli da Sauyin Yanayi da Makamashi na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) a Jihar Kaduna, Rahmatu Suleiman, ta bayyana muhimmiyar rawar da hukumar ke takawa wajen wayar da kan jama’a da kuma haɗa kai da al’umma domin hana aukuwar bala’o’i.

 

Ta ce NOA na aiki kafada da kafada da NEMA wajen isar da saƙonnin wayar da kai ga al’ummomi a faɗin jihar, inda ta bayyana cewa hukumar na da ma’aikata a dukkan ƙananan hukumomi 23 na Jihar Kaduna da ke gudanar da wayar da kan jama’a kan haɗarin bala’o’i kamar ambaliya.

Rahmatu Suleiman ta ƙara da cewa hukumar na kuma aiki tare da kafafen yaɗa labarai domin ƙara wayar da kan jama’a, inda ta bayyana cewa Daraktan NOA na Jihar Kaduna, Danjuma Makama, kan bayyana a kafafen yaɗa labarai sau da dama domin ilmantar da jama’a kan matakan kariya da kuma hanyoyin rage illolin ambaliya da sauran bala’o’i.

 

Mahalartar taron sun jaddada muhimmancin ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, shugabannin al’umma da kuma jama’a domin hana aukuwar bala’o’i da kuma tabbatar da saurin kai dauki idan suka faru.

 

Sun kuma yi kira a ci gaba da gudanar da shirye-shiryen wayar da kan jama’a domin gujewa halayen da kan jawo hatsari ko ƙara tsananta matsaloli, musamman a lokutan hatsarin tankokin mai da kuma ambaliya.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara