Connect with us

Labarai

Matasan Kauru Sun Yi Allah-wadai da Mulkin Ƙarfi, Sun Buƙaci Adalci da Haɗin Kai

Published

on

 

Daga Yusuf Zubairu

Wata ƙungiyar matasa a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa shugabanci na bai-ɗaya ba tare da nuna rinjaye a bangare daya ba, shi ne ginshikin dorewar dimokuraɗiyya da haɗin kan al’umma a yankin.

Ƙungiyar, wato Kauru Youth Ambassadors (KYA) ta yi wannan kira ne yayin mayar da martani ga kalaman wani mai suna Musa Waziri ne a wani bidiyo da ya karade kafafen yanar gizo, inda ta jaddada cewa Kauru ta ƙunshi sassa uku ne da suka hada da  Masarautar Kauru, Sarautar Kumana da Sarautar Chawai.

A cewar ƙungiyar, kowanne daga cikin waɗannan sassa uku na da masu ilimi, ƙwarewa da kishin ƙasa, waɗanda suka cancanci rike muƙamai a kowane fanni.

Da yake magana a madadin KYA, Kwamared Junaidu Ishaq Maisalati ya ce ƙungiyar ta soki ikirarin Waziri na cewa “ana ƙwace iko ne, ba a bayar da shi ba,” inda ya bayyana cewa mafi akasari  siyasa na karkata ne ga waɗanda ke da rinjayen yawan jama’a, da albarkatun kasa da damar shiga tsarin jam’iyya.

Ya bayyana cewa tsarin raba mulki (zoning) ba wajibi ba ne a harkar siyasa, illa hanya ce ta kaucewa watsi da wani yanki, tare da tabbatar da wakilci na adalci a al’umma mai bambance-bambance kamar Kauru.

Ƙungiyar ta kuma bayyana cewa ba daidai ba ne a ce tsarin karba-karba wato zoning na haifar da shugabanni marasa ƙwarewa, alhali kuma ana da tabbacin cewa akwai ƙwararru a dukkan sassan Kauru.

Ta jaddada cewa tsarin na karba-karba ba ya rage ƙa’idar shugabanci, sai dai yana ƙarfafa kowanne yanki ne ya gabatar da mafi cancantar ’ya’yansa idan aka ba shi dama.

A cewar ƙungiyar, mulki na karba karba  yana ƙarfafa tarbiyyar shugabanci, gina ƙwarewa da kuma ƙarfafa cibiyoyin siyasa.

Saboda haka, ta yi gargaɗi cewa ci gaba da keɓance wasu sassa na iya haifar da rashin yarda, sakaci da ɓacin rai, wanda hakan ke tauye ci gaba da haɗin kan al’umma.

Ƙungiyar Kauru Youth Ambassadors (KYA) ta nanata cewa ya zama wajibi a tabbatar da adalci domin samun haɗin kai, zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a Kauru.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara