Labarai
Matasa Dubu Ɗaya Za Su Samu Horon Fasahar Zamani A Nasarawa — Remi Tinubu
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa matasa dubu ɗaya (1,000) za su samu horo kan tsaron yanar gizo (cyber security) da fasahar binciken dijital (digital forensics) ta hanyar Cibiyoyin Koyon Fasahar Dijital ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) a Jihar Nasarawa.
Uwargidan Shugaban Ƙasan ta bayyana haka ne yayin bikin kaddamarwa da miƙa Cibiyar Koyon Fasahar Dijital (Digital Learning Center) a Lafia da wasu jihohin ƙasar.
Sanata Oluremi Tinubu ta ce, shirin horon matasan wanda za a rika gudanarwa a kowane mako daga yanzu har zuwa watan Disamba na shekara mai zuwa, yana da nufin yakki da laifukan yanar gizo (cyber crimes) da kuma ƙarfafa matasa su samu ƙwarewa ta yadda za su dogara da kansu a rayuwa.
Uwargidan Shugaban Ƙasan ta yaba wa Daraktan Hukumar NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, bisa ƙoƙarin gina cibiyoyi 15 na koyon fasahar dijital tare da haɗin gwiwar Renewed Hope Initiative, domin bunƙasa damar samun ilimi ta fasahar zamani a ƙasar.
A nasa jawabin, Daraktan Janar na NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, ya bayyana cewa dijitalizashan (digitalization) muhimmin ginshiƙi ne a cikin manufofin sauyin gwamnati ta yanzu, don haka aka kafa cibiyoyi 296 na koyon fasahar dijital a fadin ƙasar.
Ya ƙara da cewa a bana, NITDA tana shirin ƙara cibiyoyi 148, wanda hakan zai kai adadin cibiyoyi zuwa 586 kafin shekarar 2027.
Shi ma Daraktan Janar na Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital ta Jihar Nasarawa (NASITDA), Sani Haruna Sani, ya bayyana cewa wannan cibiya za ta zama hedikwatar horo kan ilimin dijital, tsaron yanar gizo da kuma binciken forensics a jihar.
Ya yi kira ga matasan jihar da su amfana da wannan dama domin su ƙara kwarewa a fannin fasahar zamani, su taimaka wajen ci gaban tattalin arzikin jihar da ƙasa baki ɗaya.
Aliyu Muraki, Lafia
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
