Connect with us

Fasaha

Majalisar Dattawa Ta Nemi Ministan Ilimi Ya Gurfana Gabanta

Published

on

Majalisar dattawa ta gayyaci ministan ilimi da hukumar bayar da tallafin karatu ta tarayya bisa jinkirin biyan dalibai hakkokinsu.

 

Majalisar dattawa a ranar Talata ta umurci kwamitinta kan ilimi da ya gayyaci hukumar bayar da tallafin karatu ta tarayya da kuma ministan ilimi don bayar da cikakken rahoto kan halin da daliban Najeriya ke ciki a shirye-shiryen bayar da tallafin karatu na kasa da kasa ciki har da rashin biyansu hakkokinsu.

 

Kudurin dai ya biyo bayan kudirin da Sanata Saliu Mustapha (APC Kwara ta tsakiya) ne ya dauki nauyi.

 

Sanata Mustapha a cikin kudirin ya yi kira da a gudanar da bincike cikin gaggawa tare da warware kalubalen biyan kudin makaranta da sauran matsalolin jin dadin da daliban Najeriya ke fuskanta kan shirin gwamnatin tarayyar Najeriya da kasashen waje da na kasashe renon Ingila, inda ya koka da halin da wadanda suka ci gajiyar tallafin ke fuskanta.

 

Ya bayyana cewa, wasu rahotannin da ke nuna cewa daliban Najeriya na fuskantar wahalhalu a kasashen Aljeriya, China, Morocco, Rasha da kuma Birtaniya, sakamakon rashin biyan kudin karatu da alawus din rayuwa, lamarin da ke haifar da yada labaran karya da kuma kunyata kasa.

 

Don haka Majalisar Dattawa ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta sanya takunkumin da ya dace a kan jami’an Hukumar bayar da tallafin karatu ta Tarayya da kuma Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya wadanda ke da alhakin wannan gazawar.

 

Ya kara da cewa rashin cika alkawurran da gwamnatin tarayya ta yi na kudi a karkashin wadannan yarjejeniyoyin duniya sama da watanni goma, zai kawo cikas ga walwala da ci gaban karatun daliban da abin ya shafa.

 

Bashir M/Wabbae

Labarai

Labarai1 day ago

Ziyarar Shugaba Tinubu Zuwa China Ta Yi Nasara

  Ziyarar Shugaba Tinubu zuwa China Ta Yi Nasara, da kuma Shaida Wa ‘Yan Najeriya Mazauna China, Yi Alkawarin don...

Labarai2 days ago

Sabon Tsarin Albashi: Majalisar Kano Ta Amince da Karin Kasafin Naira Biliyan 99

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙarin kasafin kudi na N99bn da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Musanta Jita-Jitar Bayar Da Kudi Ga ‘Yan Ta’adda

  Gwamnatin Jihar Zamfara tayi watsi da jita-jitar da ke yawo cewar tana shirin bayar da kudi ga wasu sanannun...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Dauki Matakan Gaggawa Don Wadata Man Fetur da Farashinsa

  Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Ɗauki Matakai Masu Ƙarfi don Magance Samuwar Man Fetur da Farashi a Faɗin Najeriya A...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nemi Hadin Gwiwar Afirka da China Don Bunkasa Tattalin Arziki

  Shugaba Bola Tinubu ya yi kira da a ci gaba da hadin kai tsakanin Afrika da Sin, yana mai...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya ta Amince da Tsare-tsare Don Yakar Rashin Abinci Mai Gina Jiki

  Daga: Bello Wakili Ministan Tsare-tsare na Lafiya da Walwala ta Jama’a na kasa, Muhammad Ali Pate, ya jaddada muhimmancin...

Labarai3 days ago

ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro

Kungiyar Tuntubar Arewa, wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce a halin yanzu, batun da ya fi damun al’ummar arewacin...

Labarai3 days ago

Hukumar NOA Ta Yabawa Majalisar Jihar Nasarawa Wajen Samarda Dokoki Masu Amfani ga Jama’a

Hukumar Wayar da Kan Jama’a da Fadakarwa ta Kasa (NOA) ta yaba wa Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa bisa ga kafa...

Kasuwanci4 days ago

Shugaba Tinubu Ya Gana da Firayim Ministan Sin, Ya Ce Afirka Na Da Damar Zuba Jari da Haɓaka

  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ce Afrika na da manyan damammaki wajen zuba jari, ci gaba, da haɓaka tare...

Labarai4 days ago

Tinubu Ya Jajantawa Jihar Yobe Kan Rashe-Rashen Rayukan da Aka Yi a Tarmuwa

  Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Yobe kan rashin rayukan da aka yi a Mafa a...

Mafi Shahara