Connect with us

Labarai

Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Published

on

Usman Muhammad Zaria 

Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa wato (National Health Fellows) a Jihar Jigawa.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala aikin, Mataimakin Darakta kuma Mai Taimaka wa Darakta-Janar na Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa, Dakta Jibrin Muhammad Bashar, ya bayyana cewa aikin daukar ma’aikatan wani shiri ne na Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya karkashin jagorancin Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate.

Dakta Bashar, wanda kuma shi ne Babban Mai Kula da aikin daukar ma’aikatan a Jihar Jigawa, ya bayyana cewa shirin na da nufin zaben Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa da za su rika sa ido kan aiwatar da Asusun Kula da Lafiya na Asali (Basic Health Care Provision Fund) a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar.

A cewarsa, wadannan ma’aikata za su kasance jakadu na Asusun Kula da Lafiya na Gwamnatin Tarayya, wanda Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Kasa (National Primary Health Care Development Agency) ke kula da shi.

Ya kara da cewa an kirkiri asusun ne domin tallafa wa rukunin al’umma masu rauni, ciki har da mata, yara da tsofaffi, ta hanyar samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya da kuma tallafin kudi.

Ya bayyana cewa za a zabi mutum ashirin da bakwai, inda kowane daya zai wakilci daya daga cikin kananan hukumomi ashirin da bakwai na Jihar Jigawa.

Dakta Bashar ya nuna gamsuwa da yadda aka gudanar da aikin daukar ma’aikatan, inda ya yaba wa kwamitin daukar ma’aikata na jihar da kwamitin  bisa kwarewa, gaskiya da kuma rashin nuna bangaranci yayin aikin.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara