Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin tarayya ta ce sauya fasalin bangaren noma a Najeriya ta hanyar bai wa samar da wadataccen abinci muhimmanci.

Ministan Noma da Wadata Kasa da Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya bayyana hakan yayin rabon kayayyakin noma ga kananan manoma a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

Ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya na aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki da dama domin bunkasa samar da ayyukan yi, da kuma rage tsadar rayuwa.

A cewarsa, Ma’aikatar Noma da  ta kaddamar da shirye-shirye da ayyuka da dama domin magance wasu matsalolin da manoma ke fuskanta, tare da tabbatar da wadatar abinci, samun sa cikin sauki, da kuma rage tsadarsa ga dukkan ‘yan Najeriya.

Ministan, wanda Daraktan Sashen Noman Lambu na Ma’aikatar Noma da Wadata Kasa da Abinci ta Tarayya, Alhaji Yarima Uba, ya wakilta, ya ce sun kuduri aniyar tabbatar da cewa dukkan shirye-shirye da tsare-tsaren bangaren noma na wannan gwamnati sun yi daidai da manufofin shugaban kasa.

Sanata Abubakar Kyari ya kara da cewa, gwamnatocin tarayya da na jihohi na ci gaba da hadin gwiwa domin magance dukkan matsalolin da ke shafar wadatar abinci.

A cewarsa, ma’aikatar na da kudurin karfafa hadin gwiwa da kungiyoyi da kamfanoni masu zaman kansu domin kara inganta kokarin tabbatar da wadatar abinci, bunkasar tattalin arziki, samar da ayyukan yi da rage talauci.

Ya nuna cewa, ma’aikatar ta tanadi aiwatar da tsare-tsare na gajeren lokaci da hanyoyin tallafi domin rage tsadar muhimman kayayyakin noma, tare da saukaka samunsu ga manoma ta hanyar tsari mai inganci da rikon amana.

Abubakar Kyari ya bukaci wadanda suka amfana da kayayyakin da su yi amfani da su yadda ya dace domin samar da karin abinci ga kasa.

Ya ce “Babban abin da muka sa a gaba shi ne saukaka samar da kayayyakin noma da na’urorin aikin gona masu inganci ga kananan manoma da tsadar wadannan kayayyaki ke hana su samun su, wanda hakan ke bukatar tallafi.”

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa kayayyakin da aka rabawa manoman kyauta sun hada da injinan noma da ake kerawa a nan gida Najeriya,  magungunan kashe ciyawa, takin zamani na ruwa, na’u’rorin feshin magani, injinan famfon ruwa, da sauransu.

An yi rabon kayayyakin ne ta hannun kungiyoyin masu noma amfanin gona daban-daban, kungiyoyin hadin gwiwar manoma, manoma masu bukata ta musamman da kuma ‘yan gudun hijira.

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara