Labarai
Gwamna Lawal Ya Buƙaci Masu Son Tsayawa Takara Su Aje Mukamansu
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya umurci dukkan ‘yan majalisar zartaswar jihar da ke son takara a zaben shekarar 2027 da su ajiye mukamansu.
Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a ranar Litinin yayin zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar a Gidan Gwamnati, Gusau.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wannan umarni ya yi daidai da dokar zabe wacce Shugaban kasa ya rattaba hannu a kai, da kuma jadawalin zaben 2027 da hukumar zabe ta kasa INEC ta fitar.
“Yau ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa na 64, inda aka tattauna muhimman batutuwa domin ci gaban Jihar Zamfara.

“A jawabin bude zaman taron, gwamnan ya umurci dukkan mambobin majalisar zartarwar da ke neman mukaman siyasa su ajiye aikinsu kafin ko a ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2026.”
Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci Sakataren Gwamnatin Jihar, da ya fitar da wata sanarwa ga dukkan jami’an gwamnati da ke da burin takara, wanda zai bukaci su ajiye mukamansu kafin ranar da aka kayyade.

Haka kuma, an umarci Shugaban Ma’aikata da ya aikawa dukkan ma’aikatan gwamnati da ke da niyyar yin takara domin su ajiye aikinsu.
Gwamna Lawal ya kara da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen hidimar al’ummar Jihar Zamfara.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
