Connect with us

Labarai

Gwamna Lawal Ya Buƙaci Masu Son Tsayawa Takara Su Aje Mukamansu

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya umurci dukkan ‘yan majalisar zartaswar jihar da ke son takara a zaben shekarar 2027 da su ajiye mukamansu.

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a ranar Litinin yayin zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar a Gidan Gwamnati, Gusau.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wannan umarni ya yi daidai da dokar zabe wacce Shugaban kasa ya rattaba hannu a kai, da kuma jadawalin zaben 2027 da hukumar zabe ta kasa INEC ta fitar.

Yau ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa na 64, inda aka tattauna muhimman batutuwa domin ci gaban Jihar Zamfara.

A jawabin bude zaman taron, gwamnan ya umurci dukkan mambobin majalisar zartarwar da ke neman mukaman siyasa su ajiye aikinsu kafin ko a ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2026.”

Sanarwar ta ce, gwamnan ya umarci Sakataren Gwamnatin Jihar, da ya fitar da wata sanarwa ga dukkan jami’an gwamnati da ke da burin takara, wanda zai bukaci su ajiye mukamansu kafin ranar da aka kayyade.

Haka kuma, an umarci Shugaban Ma’aikata da ya aikawa dukkan ma’aikatan gwamnati da ke da niyyar yin takara domin su ajiye aikinsu.

Gwamna Lawal ya kara da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da mayar da hankali wajen hidimar al’ummar Jihar Zamfara.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara