Connect with us

Fasaha

Cutuka Biyar Da Ake Ɗauka A Lokacin Zafi

Published

on

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗi a baya-bayan nan dangane da ƙaruwar yanayin zafi a sassan ƙasar, yayin da jihohi da dama suke fuskantar ƙarin matsanancin zafi.

Gargaɗin ya kuma nuna cewa, tsananin zafin da za a yi fama da shi cikin kwanaki uku ko huɗu masu zuwa wanda zai haddasa damuwar da yanayin na zafi kan haifar a jihohi goma sha tara na ƙasar daga yankin arewa ta tsakiya da yankin gabashin ƙasar.

Kan haka ne muka tuntuɓi likita domin ya yi mana ƙarin bayani game da cututtuka biyar da aka fi kamuwa da su a lokacin zafi da kuma hanyoyin kare kai.

Sanƙarau – Dakta Hassan Ibrahim, likita a asibitin Biba da ke jihar Kaduna ya ce cutar sanƙarau na faruwa ne galibi idan aka samu cunkoson jama’a a wuri ɗaya da ya haɗu da zafi.

A cewarsa, “ƙwayoyin cuta za su shiga jikin mutum sai su shafi ƙwaƙwalwa sai a samu irin wannan.”

Zazzaɓin cizon sauro – Likitan ya ce idan yanayin zafi ya zo, mutane suna yawan buɗe jikinsu domin su sha iska. Ya ce “mutane sun fi zama a waje lokacin faɗuwar rana, lokacin da sauro ke tasiri da tafiyar da maleriya.

Hakan yana yawan taso da cutar maleriya a jikin mutane, kamar yadda likitan ya faɗa.

Fesowar ƙuraje – A lokacin zafi ne ake yawan zufa lamarin da ke janyo fesowar ƙuraje a jikn mutane wanda a cewar Dakta Hassan, idan ba a kula da su ba, “aka yi irin wata sosawa, yana iya kawo ciwo da wata ƙwayar cuta za ta iya ratsawa.”

Amai da gudawa – Dakta Hassan ya ce a irin wannan lokaci na zafi ne aka fi samun ƙuda da ruɓewar abinci. Ya ce idan ba a kula da abincin da muke ci ba, aka bari ƙuda suka yi damalmala a kai, hakan zai iya kawo ciwo a ciki idan aka ci.

Ƙonewar ruwa a jiki – A irin wannan yanayin, jikin mutum na yawan bushewa musamman a tsakanin dattijai. A cewar likitan, abin da ke sa mutum ya ji ƙishirwa, idan mutum na da rauni, ba za su samu jikinsu ya ankarar da su cewa su sha ruwa ba, ana so a riƙa shan ruwa a kai a kai.

Hanyoyin kariya

Dakta Hassan Ibrahim ya ce muhimman matakan da ya kamata mutane su ɗauka wajen kare kansu daga kamuwa da cuta a lokacin zafi shi ne tabbatar da cewa ana samun yanayin “shiga da fita ta iska” ta hanyar buɗe taga a wuraren kwana da wuraren aiki da kuma rage cunkoson jama’a a wuri guda.

Ya kuma ce akwai buƙatar a riƙa amfani da gidan sauro idan za a kwanta domin kare kai daga kamuwa da cutar maleriya inda ya ce akwai buƙatar a taƙaita zama a waje da yamma.

A cewar likitan, babban matakin da ya kamata mutane su kiyaye shi ne na tabbatar da tsaftar abincin da za ake ci musamman ƴaƴan itatuwa da kuma tabbatar da tsaftar jiki.

Ƙarin wani matakin shi ne yawaita wanka a kai a kai domin rage yanayin zafi a jiki.

Sai kuma yawaita shan ruwa domin gujewa ƙonewar ruwa a jiki inda ya shawarci masu azumi da su yawaita shan ruwa da zarar sun yi buɗa baki.

Abin da ya sa aka fi kamuwa da cututtuka a yanayin zafi

Dakta Hassan Ibrahim ya bayyana cewa dalilin shi ne, galibin cututtuka sun fi haɓaka a lokacin zafi saboda yanayin tsaurin jiki da inda jiki ke tafiya.

“Jiki yana da yadda yake gyara kansa a duk yanayin da ya shiga, lokacin zafi yana zuwa masa da ƙarin matsi da yadda jikin zai fitar da zafi da inda zai riƙe daidai.” in ji likitan.

“A lokacin zafi, mun ƙara wa jikinmu aiki, saboda a ciki ɗumi gare shi kuma yana son ya riƙe ɗumi kuma a lokacin zafi, jikinmu yana ƙara aikin fitar da ɗumi waje yana kuma ƙoƙarin samun abin sanyi da zai iya daidaita yanayin da yake tafiyar da aikin.”

Likitan ya ce a irin wannan yanayi da jiki ke tsintar kansa a lokacin zafi, “akwai rauni da ke tasar da cutuka da za su yi tasiri.”

A cewar shi, kashi 90 na cututtuka a duniya yana da alaƙa da wani abu na sarari saboda akwai ƙwayoyin cuta da suka fi tasiri a yanayin zafi.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara