Labarai
BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai
Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da Harkokin Ɗalibai, Farfesa Shamsuddeen Umar, tana mai bayyana zargin a matsayin ƙarya, marar tushe kuma na ɓata suna.
Matsayar jami’ar na kunshe cikin wata sanarwa da Shugaban Sashen Kafofin Sadarwa na Dijital, Nura Garba, ya fitar a madadin Magatakardar jami’ar, sakamakon wani rubutu da Mr. Abdulrahman Abdulateef, wanda aka fi sani da MC Almajiri, tsohon ɗalibi a Sashen Ilimin Ƙasa (Geology), ya wallafa a kafafen sada zumunta.
A cewar sanarwar, jami’ar ta yi watsi da zarge-zargen baki ɗaya, tana mai jaddada cewa Farfesa Umar ya yi wa jami’ar hidima cikin kwarewa, gaskiya da ƙwarewar aiki tsawon lokacin da ya rike muƙaminsa.
Jami’ar ta bayyana cewa an tsawaita wa’adin naɗin Farfesa Umar a matsayin Dekan Harkokin Ɗalibai sau da dama, sakamakon kyakkyawan aikinsa da jajircewarsa wajen kula da walwalar ɗalibai da al’ummar jami’a gaba ɗaya.
BUK ta ƙara da cewa babu wani tarihin aikata ba daidai ba ko cin hanci da aka taɓa samu a kansa yayin gudanar da aikinsa na hukuma.
Sanarwar ta ce: “Jami’ar na kallon wannan wallafa a matsayin yunkuri na gangan domin ɓata sunan jami’a da kuma ɗaya daga cikin manyan jami’anta masu mutunci.”
Saboda haka, jami’ar ta buƙaci Abdulateef da ya gaggauta janye waɗannan zarge-zargen na ɓata suna tare da ba da haƙuri a bainar jama’a ga jami’ar da kuma Farfesa Umar.
Jami’ar ta kuma yi gargaɗin cewa rashin bin wannan buƙata zai tilasta mata ɗaukar matakin shari’a da ya dace domin kare martabarta da kuma sunan ma’aikatanta.
A ƙarshe, jami’ar ta jaddada ƙudurin ta na ci gaba da kiyaye mafi girman matakan ɗabi’a, gaskiya da ƙwarewar ilimi, tana mai cewa ba za ta lamunci duk wani aiki da zai iya raunana ƙimarta da martabarta ba.
Khadijah Aliyu
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
