Labarai
Bayan Sauya Sheƙa: Gwamna Yusuf Ya Amince da Kafa Majalisar Dattawan Kano
Daga Abdullahi Jalaluddeen
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC, inda ya jagoranci gagarumar sauya sheƙa a siyasar Jihar Kano.
Sauya sheƙar ta haɗa da mambobi 34 na Majalisar Dokokin Jihar, dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, da kuma daukacin masu riƙe da muƙaman siyasa a gwamnatinsa.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wani babban biki da aka gudanar a dakin taro na Coronation da ke Gidan Gwamnatn Kano.
Da yake jawabi a taron, Gwamna Yusuf ya ce matakin sauya sheƙar ya biyo bayan shawarwari masu zurfi da kuma tantance halin da jihar ke ciki a yanzu da burin da take da shi a gaba.
Ya bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin yin aiki tare da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, da nufin hanzarta ci gaban Kano tare da kawo ainihin amfanin dimokuraɗiyya ga al’ummar jihar.
“Bayan shawarwari masu zurfi kan makomar Jihar Kano, ni tare da mambobi 34 na Majalisar Dokoki, dukkan ƙananan hukumomi 44 da kuma dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa, mun yanke shawarar shiga jam’iyyar APC domin yin aiki da shugabanci mai hangen nesa na Bola Ahmed Tinubu,” in ji gwamnan.
Gwamna Yusuf ya ce Ajandar sabunta kudurori ta Renewed Hope ta Shugaban Ƙasa ta fara haifar da sakamako mai kyau a faɗin ƙasar, yana mai jaddada cewa Kano ba za ta iya zama a gefe ba a lokacin da haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya zai buɗe ƙarin damammaki ga al’ummarta.
Ya ƙara da cewa rikice-rikicen siyasa da faɗa ba su taimaka wa kyakkyawan shugabanci, yana mai bayyana shugabanci a matsayin hidima ga jama’a ba gasa ba.
Gwamnan ya tabbatar wa magoya bayansa cewa wannan mataki bai rage ƙoƙari da gudummawar dukkan waɗanda suka tsaya tare da shi a tafiyarsa ta siyasa ba.
Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su duba sauya sheƙar cikin adalci, yana mai jaddada cewa an ɗauki matakin ne da kyakkyawar niyya domin samar da ƙarin dama, musamman ga matasan jihar.
Haka kuma, Gwamna Yusuf ya sanar da amincewa da kafa Majalisar Dattawan Kano. Ya ce majalisar ba za ta kasance ta siyasa ba, kuma za ta zama cibiyar ba da shawara ga gwamnati domin inganta zaman lafiya, haɗin kai da kyakkyawan shugabanci a jihar.
A cewarsa, haɗin kai da Gwamnatin Tarayya zai taimaka wajen samar da yanayin siyasa mai tsafta da haɗin kai, tare da tabbatar da daidaito da kwanciyar hankali na dogon lokaci.
“Muna buɗe sabon shafi bisa ginshiƙin haɗin kai, kwanciyar hankali da shigar kowa. Ƙofofinmu a buɗe suke ga dukkan al’ummar Kano,” in ji gwamnan, yayin da ya yaba wa shugabancin APC bisa goyon baya da halartar bikin sauya sheƙar.
Manyan shugabannin APC da dama sun halarci taron, ciki har da tsohon Shugaban APC na Ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin; Karamin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane, Abdullahi Ata Fagge; Sanata Kawu Sumaila; Shugaban APC na Jihar Kano; da kuma dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, tare da sauran jiga-jigan jam’iyyar.
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
