Connect with us

Labarai

Bayan Sauya Sheƙa: Gwamna Yusuf Ya Amince da Kafa Majalisar Dattawan Kano

Published

on

Daga Abdullahi Jalaluddeen

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP zuwa  APC,  inda ya jagoranci gagarumar sauya sheƙa a siyasar Jihar Kano.

Sauya sheƙar ta haɗa da mambobi 34 na Majalisar Dokokin Jihar, dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, da kuma daukacin masu riƙe da muƙaman siyasa a gwamnatinsa.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wani babban biki da aka gudanar a dakin taro na Coronation da ke Gidan Gwamnatn Kano.

Da yake jawabi a taron, Gwamna Yusuf ya ce matakin sauya sheƙar ya biyo bayan shawarwari masu zurfi da kuma tantance halin da jihar ke ciki a yanzu da burin da take da shi a gaba.

Ya bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin yin aiki tare da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, da nufin hanzarta ci gaban Kano tare da kawo ainihin amfanin dimokuraɗiyya ga al’ummar jihar.

Bayan shawarwari masu zurfi kan makomar Jihar Kano, ni tare da mambobi 34 na Majalisar Dokoki, dukkan ƙananan hukumomi 44 da kuma dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa, mun yanke shawarar shiga jam’iyyar APC domin yin aiki da shugabanci mai hangen nesa na Bola Ahmed Tinubu,” in ji gwamnan.

Gwamna Yusuf ya ce Ajandar sabunta kudurori ta Renewed Hope ta Shugaban Ƙasa ta fara haifar da sakamako mai kyau a faɗin ƙasar, yana mai jaddada cewa Kano ba za ta iya zama a gefe ba a lokacin da haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya zai buɗe ƙarin damammaki ga al’ummarta.

Ya ƙara da cewa rikice-rikicen siyasa da faɗa ba su taimaka wa kyakkyawan shugabanci, yana mai bayyana shugabanci a matsayin hidima ga jama’a ba gasa ba.

Gwamnan ya tabbatar wa magoya bayansa cewa wannan mataki bai rage ƙoƙari da gudummawar dukkan waɗanda suka tsaya tare da shi a tafiyarsa ta siyasa ba.

Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su duba sauya sheƙar cikin adalci, yana mai jaddada cewa an ɗauki matakin ne da kyakkyawar niyya domin samar da ƙarin dama, musamman ga matasan jihar.

Haka kuma, Gwamna Yusuf ya sanar da amincewa da kafa Majalisar Dattawan Kano. Ya ce majalisar ba za ta kasance ta siyasa ba, kuma za ta zama cibiyar ba da shawara ga gwamnati domin inganta zaman lafiya, haɗin kai da kyakkyawan shugabanci a jihar.

A cewarsa, haɗin kai da Gwamnatin Tarayya zai taimaka wajen samar da yanayin siyasa mai tsafta da haɗin kai, tare da tabbatar da daidaito da kwanciyar hankali na dogon lokaci.

 

Muna buɗe sabon shafi bisa ginshiƙin haɗin kai, kwanciyar hankali da shigar kowa. Ƙofofinmu a buɗe suke ga dukkan al’ummar Kano,” in ji gwamnan, yayin da ya yaba wa shugabancin APC bisa goyon baya da halartar bikin sauya sheƙar.

Manyan shugabannin APC da dama sun halarci taron, ciki har da tsohon Shugaban APC na Ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin; Karamin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane, Abdullahi Ata Fagge; Sanata Kawu Sumaila; Shugaban APC na Jihar Kano; da kuma dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, tare da sauran jiga-jigan jam’iyyar.

 

 

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara