Connect with us

Labarai

Ana binciken gano waɗanda suka ciri miliyoyi a bankin Ethiopia

Published

on

Babban bankin kasuwancin Ethiopiya ya bai wa abokan hulɗarsa da suka ciri kuɗin da ya zarce wanda ke ajiye a asusunsu nan da ƙarshen makon nan su mayar da kuɗaɗen ko kuma su fuskanci shari’ah.

Kafafen yaɗa labarai a ƙasar sun ce fiye da dala miliyan 40 aka cira ko aka tura wasu bankuna a ranar Asabar da aka samu tangarɗa ta tsawon sa’oi a bankin na CBE.

A wata hira da BBC Newsday, shugaban bankin Abe Sano ya ce bankin ya gano akasarin hada-hadar da aka yi a lokacin da aka samu matsalar.

Da aka tambaye shi ko bankin zai kai rahoton waɗanda ba su mayar da kuɗin ba ga ƴansanda, Mista Abe ya ce “eh, eh sosai ma. Mun soma yin haka.”

Ya ƙara da cewa bankin zai ɗauki matakin shari’a kan waɗanda suka ƙi mayar da kuɗaɗen nan da ƙarshen makon nan”.

“Babu yadda za su tsira saboda abokan hulɗarmu ne. Mun san su. Za a iya gano su kuma za su yi bayanin abin da suka yi,” in ji Mista Abe.

Wasu kwastamomin da suka kwashi kuɗi mai yawan gaske tuni sun mayar wa bankin, in ji Mista Abe.

Sai dai ya ƙaryata rahotanni cewa kwastamominsu sun kwashi dala miliyan 40 inda ya ce kuɗin bai kai yawan wanda aka kwasa ba amma za a tantance yawansu bayan an gama gudanar da bincike nan gaba a makon nan.

Mista Sano ya ƙara da cewa ana yin bincike saboda wasu kwastamomi 10,000 da suka tura kuɗi lokacin da aka samu matsala sun yi haka ne kan ƙa’ida.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara