Connect with us

Labarai

Aliko Dangote ya Miƙa Korafi ga Hukumar ICPC Kan Shugaban NMDPRA Farouk Ahmed

Published

on

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya miƙa wa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Nijeriya, ICP ƙorafi kan shugaban Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Nijeriya, NMDPRA,  Ahmed Farouk, kan zarginsa da cin hanci da kuma almubazzaranci da dukiya.

A cikin takardar ƙorafin da aka gabatar a ranar 16 ga Disamba, Dangote ya nemi a kama Ahmed, a gudanar da bincike tare da gurfanar da shi a gaban ƙuliya bisa zarginsa da yin rayuwar ƙarya fiye da ƙarfinsa a matsayin ma’aikacin gwamnati.

A cikin takardar ƙorafin, wadda ofishin Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu (SAN) ya samu, Dangote ya zargi shugaban NMDPRA da kashe fiye da dala miliyan bakwai ba tare da wata shaida ta halastacciyar hanyar samun kuɗaɗen shiga ba, har na tsawon shekaru shida kafin a biya kudin makarantar ‘ya’yansa hudu a makarantu daban-daban a Switzerland.

A cikin takardar ƙorafin, wadda ofishin Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu (SAN) ya samu, Dangote ya zargi shugaban NMDPRA da kashe fiye da dala miliyan bakwai ba tare da wata shaida ta halastacciyar hanyar samun kuɗaɗen shiga ba, har na tsawon shekaru shida kafin a biya kudin makarantar ‘ya’yansa hudu a makarantu daban-daban a Switzerland.

A cikin takardar ƙorafin, Dangote ya ambaci sunayen ‘ya’yan Ahmed guda hudu da makarantunsu da ke Switzerland, ciki har da adadin da aka biya wa kowannensu don tabbatar da zarginsa da kuma neman hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta yi bincike.

Ya yi zargin cewa Ahmed yana amfani da tsarin NMDPRA don wawure da karkatar da kudaden jama’a don amfanin kai da kuma neman wata manufa ta ƙashin-kai don cutar da al’ummar Nijeriya, lamarin da ya jawo bore da ƙungiyoyi daban-daban suka yi kwanan nan.

Dangote ya yi iƙirarin cewa a tsawon rayuwar shugaban NMDPRA a matsayinsa na ma’aikacin gwamnati a Nijeriya duka abin da ya samu ko dala miliyan bakwai bai kai ba.

Ɗan kasuwan ya ce ana zargin an karkatar da kuɗin daga asusun gwamnati don biyan kuɗin karatun ‘ya’yansa a ƙasashen waje.

‘Yin abin da ya dace’

“Babu shakka gaskiyar da ke sama game da cin amanar ofis, karya Dokar Ɗa’a ga jami’an gwamnati, azurta kai daga cin hanci da rashawa, da almubazzaranci babban laifi ne na cin hanci da rashawa wanda Hukumarku (ICPC) ta ba da iko bisa doka a ƙarƙashin sashe na 19, na Dokar ICPC don bincike da gurfanarwa,” in ji Dangote.

“Bayan nasarar gurfanar da irin wannan mutumin, a ƙarƙashin sashe na 19 na Dokar ICPC, mutumin zai fuskanci ɗaurin shekaru biyar ba tare da zaɓin tara ba.

“Muna da ƙarfin hali mu bayyana cewa ICPC tana da matsayi mai kyau tare da hukumomin ‘yan’uwanta don gurfanar da laifukan kuɗi da sauran laifukan da suka shafi cin hanci da rashawa, kuma bayan kafa shari’ar farko, Kotuna ba sa jinkirin hukunta masu laifi.

Dangote ya yi alƙawarin gabatar da hujjoji don tabbatar da zarginsa na wadaƙar da Ahmed ke yi da azurta kansa da cin amanar aikinsa.

‘Yan Nijeriya na buƙatar su san gaskiya’

“Na sha jin mutane da ke korafi game da wani ma’aikacin gwamnati wanda ya sanya ‘ya’yansa a wata makarantar sakandare, inda a cikin shekaru shida aka kashe wa hudu daga cikinsu dala miliyan biyar daga kuɗaɗen Nijeriya,” in ji shi a wani taron manema labarai a Matatar Dangote da ke yankin Ibekku-Lekki na Jihar Legas.

“‘Ya’yana sun je makarantar sakandare a Nijeriya. Ba su je wata ƙasa daban don halartar makarantar sakandare ba.”

A ranar Talata, Dangote ya wallafa cikakkun bayanai game da zarge-zargen a wata jarida kuma bayan awanni kadan ya miƙa takardar ƙorafi kan shugaban NMDPRA.

Shugaban Matatar Dangote ya ce, “‘Yan Nijeriya sun cancanci sanin tushen wadannan kudaden da wani jami’in gwamnati ya biya yayin da iyaye da yawa a jiharsa ta Sokoto ba za su iya biyan kudin makaranta na N10,000 ga ‘ya’yansu da unguwanninsu ba.”

Ya zargi hukumar da kawo cikas ga kokarin inganta matatun man fetur na gida musamman tare da ci gaba da bayar da lasisin shigo da kaya.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara