Connect with us

Labarai

Adalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari

Published

on

Masu ruwa da tsaki daga masarautun gargajiya na Kumana da Chawai a Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna sun amince da wani tsarin raba mukamai na siyasa da nufin magance rashin daidaito da aka dade ana fama da shi a yankin.

Wannan matsaya ta samu ne bayan tarurrukan da aka gudanar a ranakun 26 da 27 ga watan Maris, 2026, inda aka gabatar da shawarar juyawar mukamai na siyasa tsakanin manyan rukuni uku na yankin, wato Masarautar Kauru, Masarautar Kumana da Masarautar Chawai.

A karkashin wannan tsari, an ware kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya ga Masarautar Kauru, kujerar Majalisar Dokokin Jiha ga Masarautar Chawai, yayin da kujerar Shugaban Karamar Hukuma aka bai wa Masarautar Kumana.

Masu ruwa da tsaki daga Kumana da Chawai sun yaba da rawar da dattawan al’umma, tsofaffin jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki suka taka a tattaunawar, suna mai cewa wannan mataki wani yunkuri ne na gina hadin kai da zaman lafiya a Kauru.

Sai dai, wannan matsaya ta jawo suka daga wani bangare na masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar APC a yankin.

Wannan bangare, karkashin jagorancin wani Zakka Peter da S.M. Taggah, ya nuna adawa da tsarin raba mukaman, inda suka goyi bayan sake zaben tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya, Muktar Zakari Chawai, da kuma dan majalisar dokokin jiha, Haruna Barnabas Danmaigona.

Sun bayyana cewa ya kamata a bar zabin shugabanni ga muradin jama’a ta hanyar dimokuradiyya maimakon tsarin raba mukamai.

A martaninsu, kungiyar KYA, wato  Kauru Youth Ambassadors wanda Junaidu Ishaq Maisalati ke jagoranta ta jaddada cewa tsarin raba mukamai hanya ce halal a dimokuradiyya domin tabbatar da adalci da hana wata kabila ko bangare mamaye iko.

Sun kuma yi nuni da sakamakon zaben 2023, inda suka ce sakamakon ya nuna yadda jama’a ke kallon yadda shugabanci ya gudana a yankin.

KYA ta yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a Karamar Hukumar Kauru da su fifita hadin kai da cigaban al’umma gaba daya fiye da muradun bangarori.

Har ila yau, ta bukaci Gwamnatin Jihar Kaduna da ta mara baya ga shirye-shiryen da ke inganta hadin kai da tabbatar da adalci wajen shiga harkokin siyasa.

Kungiyar ta jaddada cewa wannan tsarin raba mukamai shi ne matakin farko na kokarin karfafa dimokuradiyya da tabbatar da daidaitaccen wakilci a Kauru.

Daga: Yusuf Zubairu

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara