Labarai
Adalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
Masu ruwa da tsaki daga masarautun gargajiya na Kumana da Chawai a Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna sun amince da wani tsarin raba mukamai na siyasa da nufin magance rashin daidaito da aka dade ana fama da shi a yankin.
Wannan matsaya ta samu ne bayan tarurrukan da aka gudanar a ranakun 26 da 27 ga watan Maris, 2026, inda aka gabatar da shawarar juyawar mukamai na siyasa tsakanin manyan rukuni uku na yankin, wato Masarautar Kauru, Masarautar Kumana da Masarautar Chawai.
A karkashin wannan tsari, an ware kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya ga Masarautar Kauru, kujerar Majalisar Dokokin Jiha ga Masarautar Chawai, yayin da kujerar Shugaban Karamar Hukuma aka bai wa Masarautar Kumana.
Masu ruwa da tsaki daga Kumana da Chawai sun yaba da rawar da dattawan al’umma, tsofaffin jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki suka taka a tattaunawar, suna mai cewa wannan mataki wani yunkuri ne na gina hadin kai da zaman lafiya a Kauru.
Sai dai, wannan matsaya ta jawo suka daga wani bangare na masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar APC a yankin.
Wannan bangare, karkashin jagorancin wani Zakka Peter da S.M. Taggah, ya nuna adawa da tsarin raba mukaman, inda suka goyi bayan sake zaben tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya, Muktar Zakari Chawai, da kuma dan majalisar dokokin jiha, Haruna Barnabas Danmaigona.
Sun bayyana cewa ya kamata a bar zabin shugabanni ga muradin jama’a ta hanyar dimokuradiyya maimakon tsarin raba mukamai.
A martaninsu, kungiyar KYA, wato Kauru Youth Ambassadors wanda Junaidu Ishaq Maisalati ke jagoranta ta jaddada cewa tsarin raba mukamai hanya ce halal a dimokuradiyya domin tabbatar da adalci da hana wata kabila ko bangare mamaye iko.
Sun kuma yi nuni da sakamakon zaben 2023, inda suka ce sakamakon ya nuna yadda jama’a ke kallon yadda shugabanci ya gudana a yankin.
KYA ta yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a Karamar Hukumar Kauru da su fifita hadin kai da cigaban al’umma gaba daya fiye da muradun bangarori.
Har ila yau, ta bukaci Gwamnatin Jihar Kaduna da ta mara baya ga shirye-shiryen da ke inganta hadin kai da tabbatar da adalci wajen shiga harkokin siyasa.
Kungiyar ta jaddada cewa wannan tsarin raba mukamai shi ne matakin farko na kokarin karfafa dimokuradiyya da tabbatar da daidaitaccen wakilci a Kauru.
Daga: Yusuf Zubairu
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
