Connect with us

Labarai

Kotu Ta Baiwa EFCC Umurnin Cigaba Da Tsare Emefiele

Published

on

Babbar kotu a Ikeja da ke jihar Legas ta bayar da umarnin ci gaba da tsare tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele.

Za a ci gaba da tsare Emefiele a hannun hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin kasa ofzagon ƙasa har zuwa ranar 11 ga watan Afrilu da kotu za ta yanke hukunci kan ba shi beli.

Tun farko da ya bayyana a kotun, tsohon gwamnan babban bankin Najeriyar ya musanta sabbin tuhume-tuhumen da ake masa na karya dokokin da suka shafi hada-hadar kuɗaɗen waje da hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin ƙasa take masa.

EFCC ta zargi Emefiele da ware wasu kuɗaɗen waje kusan dala biliyan biyu ba tare da bin ka’ida ba.

Wannan na cikin tuhume-tuhume 26 da ake masa a ƙarar da aka gabatar gaban babbar kotun da ke Ikeja.

Matakin ya ƙara ta’azzara taƙaddamar shari’a tsakanin EFCC da tsohon gwamnan babban bankin wanda kuma yake fuskantar tuhuma kan almundahana da rashawa da haɗa baki wajen aikata laifi a Abuja, babban birnin Najeriya.

Emefiele, wanda ya bayyana gaban babbar kotu a Legas karƙashin mai shari’a Rahman Oshodi, ya musanta aikata zarge-zargen da ake masa.

An karanto masa tuhume-tuhume 26 da ake masa da wanda ake kararsu tare Henry Omoile.

Dukkansu sun musanta zarge-zargen da ake masu.

Sun kuma nemi kotu ta bayar da su beli zuwa lokacin da za a saurari ƙara.

Lauyan Emefiele, Lebi Lawal ya ce ya kamata kotu ta duba matsayin wanda yake karewa.

A cewar lauyan, “tsawon shekara tara, Emefiele ne ma’aikacin banki na ɗaya a Najeriya.

Lauyan ya kuma roƙi kotu ta sake nazari kan ɗabi’un Emefiele tun bayan kama shi.

Bayan hawansa kan mulki ne, shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya dakatar da Emefiele daga shugabancin babban bankin ƙasar.

Makonni bayan dakatar da shi ne kuma aka kama shi tare da gurfanar da shi gaban shari’a a watan Nuwamba kan zarge-zargen almundahana.

Labarai

Labarai19 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai21 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai22 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi22 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara