Labarai
Matasa sun fara hakura da shan miyagun kwayoyi: – NDLEA
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kwara, ta ce za ta kara karfafa matasa su shiga wasannin motsa jiki domin rage sha da safarar miyagun kwayoyi a tsakanin su.
Kwamandan NDLEA na jihar, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da mambobin kungiyar marubuta wasanni (SWAN) a Ilorin babban birnin jihar Kwara.
A cewarsa, sun dauki matakin bayan kalubalen da ake fuskanta a baya-bayan nan na aikin ‘yan masu safarar miyagun kwayoyi a jihar.
Ya ce kamar yadda matasa ke amfani da muggan kwayoyi yana sa su kara kaimi wajen yaki da wannan mummunan dabi’a.
Kwamanda Ibrahim ya nuna damuwarsa kan zargin da ake yi na sayar da miyagun kwayoyi da da masu kula da ‘yan wasa ke yi.
Ya kuma ce hukumarsa ta samu a nasara a baya-bayan nan ne na samun hukuncin daurin rai da rai kan wani koci da aka kama yana sayar da kwayoyi ga matasa ‘yan wasa da yake kula da su.
A nasa jawabin shugaban kungiyar marubuta wasanni ta Najeriya SWAN reshen jihar Kwara, Ayodeji Ismail ya bayyana cewa marubutan wasanni suna da masaniya kan illolin da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa.
Ya kuma bada tabbacin cewa kungiyar zata sake horas da ‘ya’yan kungiyar domin bayar da rahoton illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.
COVALI MUHAMMAD RABIU/Wababe
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana