Connect with us

Fasaha

‘Yan Sanda Sun Kama Direban Da Ya Dauki Bajimi A Kujerar Fasinja

Published

on

Jami’an ’yan sanda sun kama wani direba mai suna Lee Meyer saboda daukar bajimi a kujerar fasinja ta gaba wadda aka kebe don dan Adam.

Bajimin nau’in Watusi mai girman kaho ’yan sandan birnin Norfolk a Gundumar Nebraska da ke Amurka ne suka kama direban bayan samun korafin da aka yi musu game da bajimin da mutumin ya dauka, in ji kafar labarai ta News Channel Nebraska.

Lee Meyer mazaunin garin Neligh—yana tuki tare da bajimi mai suna Howdy Doody, a kowace hanyar.

Hukumomin da suke kula da hanyoyi a yau da kullun kuma sun ga alama mai launin rawaya a gefen motar bayan sun duba sai ga bajimin a ciki.

“Jami’an sun samu kiran waya da ke nuna wata mota na shiga garin tare da saniya,” kamar yadda Kyaftin din ’Yan sanda Chad Reiman ya shaida wa tashar.

“Sun yi tunanin cewa zai zama dan maraki ne, ko wani karamin dabba ko wani abu da zai shiga cikin motar.

“Sakamakon haka, jami’in ya umarci jami’in da ke kula da hanyar ya dakatar da motar saboda dalilin tsaro,” in ji Reiman.

Reiman ya ci gaba da cewa, “Akwai wasu batutuwa masu muhimmanci game da wannan hali.

Jami’in ya zabi ya rubuta masa gargadi kuma ya roke shi ya dauki bajimin ya koma gida ya bar birnin.

“Ban san dalilin da ya sa yake yin hakan ba a ranar,” Reiman ya bayyana wa kafar labarai ta People.com

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara