Labarai
Alhazai Za Su Biya Miliyan Bakwai Don Sauke Farali
Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bukaci maniyyatan aikin Hajjin bana da su biya karin Nera Miliya Daya da Dubu Dari Tara kan kudaden da suka biya a baya.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ta fito da yammacin ranar Lahadi mai dauke da sa hannun mataimakiyar daraktar hulda da jama’a ta hukumar, Fatima Sanda Usara.
Fatima Usara ta kara da cewa hukumar ta kuma bada wa’adin ranar 29 ga Maris a matsayin ranar da za a kammala bada cikon kudin.
Ta ce hakan ya zama wajibi duba da yadda darajar Naira ke faduwa a kowacce rana.
A baya dai hukumar ta tsayar da naira miliyan 4 da dubu dari 5 a matsayin kudin aikin Hajjin, kafin daga bisani ta kara naira dubu dari 4, ya zama naira miliyan hudu da dubu 9, sai kuma yanzu da ta sanar da karin kusan naira miliyan biyu.
Idan har wannan kari ya tabbata a yanzu, farashin kujerar aikin hajji zai tashi kan Naira miliyan 6 da dubu dari 9.
A watan Fabarairun da ya gabata ne Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Najeriya ta kayyade kusan naira miliyan biyar a matsayin kudin kuejrar hajjin bana.
Sai dai tun bayan lokacin, hukumar ta soma tababar kara wa maniyyatan kudi bisa dalilan faduwar darajar naira.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United