Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Published

on

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu.

Jakadan Qatar a Najeriya Dr.  Ali Bn Ghanem Al-Hajari, ya yi wannan alkawarin  a yayin bikin kaddamar da ginin sabuwar makarantar firamare a Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Ya bayyana cewa ilimi na da matukar muhimmanci wajen farfado da jihar da rikuci ya daidaita.

Jakadan wanda ya kaddamar da ginin tare da gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya jaddada cewa  idan aka kammala  za a  samar da kayan aiki na zamani don baiwa marayu damar koyo a kyakkyawan yanayi.

Gwamnatin Qatar za ta bayar da muhimmin tallafi ga marayu kusan 1000 a jihar Borno, za mu kuma ba da muhimmanci ga shirin gwamnati na samar da ingantaccen yanayin koyo ga yaran da rikicin Boko Haram ya daidaita.” Inji Ghanem.

Tunda farko Ambasada Ali Bn Ghanem Al-Hajari da mukarrabansa sun kai ziyarar ban girma ga Gwamna Babagana Zulum a fadar gwamnati inda ya sake jaddada aniyar kasarsa na taimakawa jihar Borno.

Gwamna Zulum ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin Qatar bisa tallafin tare da ba da tabbacin samar da yanayi mai kyau don samun ilimi mai inganci.

A watan Janairun bana ne gwamnan ya aza harsashin ginin gidan marayu da kungiyar agaji ta Qatar Charity Organisation ta gina.

Jakadan ya samu rakiyar mataimakinsa, Mista Abdullah Hilal Alnuimi, da daraktan kungiyar agaji ta Qatar Hamdi Abdou.

 

Dauda Iliya

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara