Connect with us

Ilimi

Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya reshen Jihar Kebbi ta tabbatar da sace dalibai ashirin da biyar daga Makarantar Sakandare ta ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Maga a Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu.

Lamarin ya faru ne a daren Litinin da misalin ƙarfe 4 na safe a lokacin da ƴan bindiga suka mamaye makarantar, inda suka kashe wani ma’aikaci ɗaya tare da jikkata wani.

A cewar wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan, CSP Nafi’u Abubakar Kotarkoshi ya sanya wa hannu, maharan ɗauke da makamai masu ƙarfi sun kutsa makarantar inda suka yi musayar wuta da jami’an tsaro da ke bakin aiki. Duk da ƙoƙarin jami’an, an ruwaito cewa maharan sun haye katangar makarantar suka kuma yi awon gaba da ɗaliban daga ɗakunan kwanan su.

Jami’in ya tabbatar da cewa Hassan Makuku wanda rahotanni suka ce shi ne mataimakin shugaban makarantar ya rasa ransa yayin harin, yayin da wani Ali Shehu ya samu rauni sakamakon harbinsa da bindiga a hannunsa na dama.

Bayan faruwar lamarin, sanarwar ta ce Kwamishinan ‘Yan Sanda, Bello Muhammad Sani, ya tura jami’an ‘yan sanda na musamman tare da jami’an soji da ƙungiyoyin ‘yan bijilanti zuwa yankin.

Tawagar haɗin gwiwa na ci gaba da bincike a hanyoyin da ake zargin maharan sun bi da dazuzzukan da ke kewaye domin gudanar da aikin ceto da kuma kama waɗanda suka aikata laifin.

Kwamishinan ya yi kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da kasancewa masu lura da muhallinsu, yana tabbatar musu da cewa rundunar za ta ci gaba da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

Sani Haruna Dutsinma

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara