Connect with us

Labarai

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Published

on

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar Hilux ga Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya, reshen Saminaka, domin ƙarfafa tsaro da kuma inganta zaman lafiya a yankin.

Wannan kyauta na da nufin tallafa wa ƙoƙarin da ake yi na tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa, musamman a cikin Masarautar Saminaka.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Shugaban kungiyar, Ma’ajin na SAPPEF, Alhaji Adamu Nuhu, ya bayyana cewa wannan gudummawa na daga cikin jajircewar ƙungiyar wajen inganta tsaron al’umma da kuma tallafa wa hukumomin tsaro.

Ya ƙara da cewa tsaro shi ne babban abin da kungiyar ke ba fifiko, kuma za su ci gaba da haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Da yake jawabi yayin bikin miƙa gudummawar, mai martaba Sarkin Saminaka, Musa Mohammed Sani, ya nuna godiya ga kungiyar bisa wannan kyakkyawan mataki.

Ya bayyana cewa wannan gudummawa ta zo a kan lokaci, yana mai cewa gyarawa da inganta motar Hilux ɗin zai taimaka wajen inganta ayyukan tsaro da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin ‘yan sanda da al’umma.

Sarkin ya kuma buƙaci sauran ƙungiyoyi da daidaikun mutane da su yi koyi da wannan mataki na tallafa wa hukumomin tsaro.

Haka kuma, Limamin Babban Masallacin Mangorori na Saminaka, Malam Shuaibu Yahaya, ya yi addu’o’in samun ci gaba da zaman lafiya, haɗin kai, da kuma shiriya daga Allah ga duk masu ruwa da tsaki.

Yusuf Zubairu/Sani Y

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara