Labarai
Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar Hilux ga Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya, reshen Saminaka, domin ƙarfafa tsaro da kuma inganta zaman lafiya a yankin.
Wannan kyauta na da nufin tallafa wa ƙoƙarin da ake yi na tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa, musamman a cikin Masarautar Saminaka.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Shugaban kungiyar, Ma’ajin na SAPPEF, Alhaji Adamu Nuhu, ya bayyana cewa wannan gudummawa na daga cikin jajircewar ƙungiyar wajen inganta tsaron al’umma da kuma tallafa wa hukumomin tsaro.

Ya ƙara da cewa tsaro shi ne babban abin da kungiyar ke ba fifiko, kuma za su ci gaba da haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Da yake jawabi yayin bikin miƙa gudummawar, mai martaba Sarkin Saminaka, Musa Mohammed Sani, ya nuna godiya ga kungiyar bisa wannan kyakkyawan mataki.
Ya bayyana cewa wannan gudummawa ta zo a kan lokaci, yana mai cewa gyarawa da inganta motar Hilux ɗin zai taimaka wajen inganta ayyukan tsaro da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin ‘yan sanda da al’umma.
Sarkin ya kuma buƙaci sauran ƙungiyoyi da daidaikun mutane da su yi koyi da wannan mataki na tallafa wa hukumomin tsaro.
Haka kuma, Limamin Babban Masallacin Mangorori na Saminaka, Malam Shuaibu Yahaya, ya yi addu’o’in samun ci gaba da zaman lafiya, haɗin kai, da kuma shiriya daga Allah ga duk masu ruwa da tsaki.
Yusuf Zubairu/Sani Y
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
